Hirarmu da Fiddausi, wata baiwar Allah da rayuwa ta jarabta cikin ɗan lokaci kaɗan. Ta rasa mahaifinta, bayan kwanaki 39 kacal kuma Allah Ya yi wa mahaifiyarta rasuwa, daga bisani ta sake rasa mijinta, aka bar mata yara guda uku cikin ƙaddarar Ubangiji. 😢🤲
Wannan ba kawai labari bane na baƙin ciki, labari ne mai ɗauke da darasi, haƙuri da ƙarfin imani. Duk da irin waɗannan ƙalubale, Fiddausi ta ci gaba da rayuwa da jajircewa, tana dogaro ga Allah da fatan alheri. ❤️
A cikin wannan interview ɗin, za ku ji abubuwa masu taɓa zuciya, darussan rayuwa da kuma muhimmancin kyautatawa iyaye tun suna tare da mu. Rayuwa tana canzawa cikin lokaci kaɗan. ✨
🎬 Ku kasance tare da mu a Rayuwata Talk Show domin kallon cikakkiyar hirar mai cike da tausayi da darasi.
📺 Tubless Media Concept